✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kama dan bindigar Katsina zai kafa sansani a Kano

Dubunsa ta cika bayan ya gudo daga yankin Malumfashi da makamai da kuma dabbobin sata

’Yan sanda sun cafke wani dan bindiga inda suka kwato shanun sata 55 a hannunsa a Karamar Hukumar Karaye ta Jihar Kano.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Kano, Usaini Muhammad Gumel, ya bayyana cewa ɗan ta’addan ya tabbatar musu cewa dubunsa ta cika ne a yayin da yake kokarin dawowa jihar Kano da zama.

Dan bindigar, wanda ba a bayyana sunansa ba, ya ce, ya gudo ne daga sansanin ’yan bindiga ta Maidaro ne da ke Malumfashi a Jihar Katsina, ya biyo ta Birnin Gwari a Jihar Kaduna ya shigo Kano.

Ya kuma bayyana cewa ya gudo daga Malumfashi ne sakamakon fadan gungunsu sa na jagoran ’yan bindiga Boderi Isiya.

A cewar dan ta’addan, an kashe jagoran bangarensu da mataimakinsa a fadan, shi ne ya gudo da shanu 55 da tumaki shida da bindigogi uku kirar AK-47, zai koma dajin kananan hukumomin Karaye da Gwarzo na Jihar Kano da zama.

Kwamishinan ’yan sandan ya shaida wa ’yan jarida a ranar Litinin cewa wanda ake zargin ya tabbatar wa ’yan sanda masu bincike cewa an sha zuwa da shi yin garkuwa da mutane a jihohin Katsina da Zamfara da kuma Kaduna.

Ya ci gaba da cewa ana farautar sauran ’yan bindigar da suka tsere domin su fuskanci hukunci.