✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Za a fara kamen iyayen da ’ya’yansu ba sa zuwa makaranta a Edo

Za a kuma hukunta duk iyayen da aka kama 'ya'yan nasu

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya ce za a fara kame tare da hukunta iyayen da yaransu ba sa zuwa makaranta daga ranar 12 ga watan Satumba mai zuwa.

Ya bayyana hakan ne ranar Litinin a Benin, babban birnin jihar lokacin da yake yawabi kan matakan da aka dauka kan shirye-shiryen komawar sabon zangon karatu mai kamawa.

Gwamna Obaseki ya kuma ce tuni aka kafa kotuna na musamman domin hukunta wadanda ke cin zarafin mata a makarantun jihar.

“Idan muka kama kowanne yaro dan kasa da shekara 18 ana amfani da shi wajen aikatau, za a hukunta iyayensa. Muna godiya ga Babban Jojin jiharmu saboda samar da kotuna na musamman da za su hukunta irin masu cin zarafin yara a makarantunmu.

“Kazalika, daga ranar 12 ga watan Satumban 2022, lokacin da makarantu za su koma, duk yaran da aka kama suna gararamba ko talla a kan tituna lokacin makaranta, za mu kama iyayensa sannan mu dauki tsattsauran mataki a kan su.

“Mun horar da mutane da za su sa ido a kan cin zarafin yara a jihar Edo,” inji shi.

Gwamnan ya kuma ce ya umarci Ma’aikatar Ilimin jihar da ta rusa duk wani ginin da ya tsufa a cikin makarantu, tare da kai daliban wasu makarantun har zuwa lokacin da za a kammala gyare-gyaren.