✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan sanda sun bankaɗo maɓoyar IPOB a Imo, sun ƙwato makamai

Rundunar ta tabbatar da aniyarta na ci gaba da yaƙi da aikata laifuka a jihar.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Imo da ke Kudu, ta gano maɓoyar wasu da ake zargin ’yan ƙungiyar IPOB da ESN ne, waɗanda ke da hannu a harkokin ta’addanci da garkuwa da mutane a jihar.

Rundunar ta ce ta ƙwato makamai masu hatsari a samamen da ta kai a maɓoyar tasu.

Kakakin rundunar, DSP Okoye Henry, ya shaida wa manema labarai cewa sun samu wannan nasara ne bisa jagorancin Kwamishinan ’yan sandan jihar.

Ya ce rundunar ta gano maɓoyar ne, domin wanzar da zaman lafiya da tsaro a jihar.

Ya bayyana cewa an kama wasu da ake zargi da garkuwa da mutane don karɓar kuɗin fansa da kuma aikata laifuka a jihar.

A cewarsa, tun watanni shida da suka gabata, rundunar ke aiki kafaɗa da kafaɗa da sauran jami’an tsaro domin yaƙar masu aikata laifuka a faɗin jihar.

Ya ce zuwa yanzu sun kama mutum 2,785 da ake zargin suna da hannu wajen haddasa rikice-rikice da sace-sacen mutane a Jihar Imo.

DSP Henry, ya ƙara da cewa waɗanda aka kama, an same su da makamai ciki har da bindigogi masu sarrafa kansu, AK-47 da bindigar da ake harbo jirgin sama da wasu kaya masu hatsari.

Haka kuma, an gano tutar ƙungiyar Biyafara da wasu kayan tsafi a cikin maɓoyar.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kai farmaki da daƙile duk wara barazana gamw da zaman lafiya da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’ar.