✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

’Yan bindigar da suka sace dan siyasa a Bauchi na neman fansar N100m

'Yan bindigar sun yi awon gaba da shi cikin dare.

‘Yan bindiga na neman kudin fansar naira miliyan 100 kan matashin dan siyasar da suka sace a Karamar Hukumar Bogoro a Jihar Bauchi, Musa Markus Masoyi, bayan shafe wata guda a hannunsu.

Aminiya ta gano cewar ‘yan bindigar sun kai farmaki Sakatariyar Kauyen Boi da ke Karamar Hukumar Bogoro a Jihar Bauchi cikin dare, inda suka yi awon gaba da matashin wanda shi ne babban makasudin zuwansu.

Wani mazaunin kauyen da bukaci a sakaya sunansa, ya ce ‘yan bindigar sun shiga ne a daidai lokacin da kowa ke barci, suka tafi da wanda aka yi garkuwa da shi zuwa wani wuri da ba a san inda yake ba.

A cewarsa, an yi awon gaba da dan siyasar ne tare da dan uwansa wanda daga baya aka sake shi a cikin daji, inda wasu mutane suka nuna masa hanyar komawa gida.

Kafin sace shi, Markus Masoyi ya taka rawar gani a taron gangamin jam’iyyar PDP da aka kammala domin nuna goyon bayansa ga jam’iyyar a Zaben 2023 mai zuwa.

‘Yan bindiga na ci gaba da kai hare-hare a wasu jihohin Arewa, inda dubban mutane suka rasa rayukansu, wasu kuma suka sauya matsugunni don tsira da rayukansu.