✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Yadda za a dandake masu fyade a Kaduna

Hukuncin kisa ta tabbata a kan masu yi wa yara fyade a Kaduna

Sabuwar dokar da Majalisar Dokokin Jihar Kaduna ta yi ta tanadiy hukuncin dandakewa da kuma kashe masu fyade a Jihar.

A ranar Laraba Majalisar ta amince da kwaskwarimar da ta yi wa Dokar Penal Code, bisa bukatar Gwamna Nasir El-Rufai, na tsananta hukuncin fyade wanda a baya daurin rai-da-rai ne a Jihar.

Shugaban Kwamitin Sadarwa na Majalisar, Tanimu Musa Kachia ya bayana wa Aminiya cewa sabbin tanade-tanaden dokar.

“Dun wanda aka kama da laifin yi wa yaro dan kasa a shekara 14 fyade to za a dandake shi a kuma kashe shi.

“Duk wanda ya yi jima’i da yaro dan kasa da shekara 14 to za a yanke masa hukuncin dandakewa da kuma kisa.

“Idan aka kama mace da laifin yi wa yaro fyade to kotu za ta yanke mata hukuncin bilateral salpingectomy sannan a kashe ta.

“Idan wanda aka yi wa fyaden ya haura shekara 14, to za a yi wa mai fyaden dandaka da daurin rai-da-rai.

“Idan wanda ya yi fyaden karamin yaro ne, to kotu za ta ba da umarnin a sanya sunasa a rajistar masu manyan laifuka sannan Antoni Janar ya wallafa a kafafen yada labarai.

“Idan shari’ar fyaden ta shafi yara ‘yan kasa da shekara 14 ne, to wajibi ne a bukaci rahoton asibiti”, inji shi.