✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Wata mata ta kashe jikarta da duka

Ta je makaranta karbar kudin da ta biya wa jikar tata da ta kashe da duka

Jami’an Hukumar Yaki da Safarar Mutane (NAPTIP) sun cafke wata mata bisa zargin kashe jikarta ’yar shekara uku da duka.

Mai magana da yawun NAPTIP, Mista Anthony Okafor, ya ce sun kama wacce ake zargin ne bayan da hukumar makarantar da yarinyar ke zuwa ta kwarmata musu abin da ya faru ranar Alhamis a Awka, babban birnin Jihar Anambra.

An damke matar ne a makarantar su yarinyar a daidai lokacin da ta yi kokarin karbar kudin makarantar da ta riga ta biya wa jikar tata.

Ya zuwa hada wannan labari, babu wani cikakken bayani kan dalilin da ya sa matar daukar wannan danyen hukunci kan jikar tata.

A cewar jami’in, “Da aka tambaye ta game da yarinyar, sai ta ce ta mutu. Ta ce yarinyar jikarta ce kuma shekarunta uku da haihuwa.

“Wacce ake zargin ta jagoranci jami’an NAPTIP zuwa inda ta boye gawar yarinyar.

“Ko da aka isa wurin, sai aka tarar ta nannade gawar cikin wata bakar jakar leda sannan ta jefar cikin ciyawa.

“An ce tun ranar 29 yarinyar ta mutu, kuma an mika matar ga ’yan sanda don ci gaba da bincike,” in ji shi.