✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tsohon Ministan Kwadago Musa Gwadabe ya rasu

Za a yi jana'izarsa a layin Madaka da ke kan tittin Maiduguri da Kano da misalin karfe 2 na rana

Allah Ya yi wa tsohon Ministan Kwadago kuma tsohon Sakataren Gwamnatin Jihar Kano, Alhaji Musa Gwadabe, rasuwa

Ahaji Musa Gwadabe ya rasu ne a kafin wayewar garin ranar Laraba bayan fama da jinya yana da shekaru 87 a duniya.

Za a gudanar da jana’izarsa a gidansa da ke daura da tittin Maiduguri da Kano da misalin karfe 2 na rana.

Marigayin ya rasu ya bar mata biyu da ’ya’ya 11 da kuma jikoki.

Daga cikin ’ya’yansa akwai Alhaji Nazifi Musa Gwadabe, wanda dan kwangila ne a Jihar Kano.

Alhaji Musa Gwadabe ya kasance minista a zaman mulkin shugaba Olusegun Obasanjo daga 1999 zuwa 2003 kuma shi ne Sakataren Gwamnatin Jihar Kano a zamanin marigayi Alhaji Sabo Sabo Bakin Zuwo.

Hakazalika a lokacin rayuwarsa ya kasance mamba a kwamitin amintattu a lokuta daban-daban, kuma ya ta taba zama Shugaban Gwamnatin Daraktoci na Hukumar ITF.