✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tsohon Hadimin Ganduje zai tsaya takarar Gwamnan Kano

Zai yi takara a karkashin inuwar jam'iyyar PRP.

Tsohon hadimin gwamnan Jihar Kano na musamman kan yada labarai a kafofin sadarwar zamani, Salihu Tanko Yakasai, ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan Jihar Kano a zaben 2023 da ke tafe.

Yakasai ya bayyana hakan ne cikin wani sako da ya wallafa ranar Talata a shafinsa na Twitter.

Tsohon hadimin gwamnan wanda aka fi sani da Dawisu ya ce zai ayyana takararsa a hukumance ranar Juma’a mai zuwa.

Wannan na zuwa ne makonni bayan ficewarsa daga jam’iyyar APC, inda ya sauya sheka zuwa jam’iyyar PRP.

Idan ba a manta ba dai a watan Fabrairun 2021 ne gwamna Ganduje ya sauke shi daga mukaminsa bisa dalilinta na cewa Yakasan na maganganun da ba su kamata ba da kuma sukar shugaban kasa Muhammadu Buhari.