✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Tinubu ya dawo Najeriya kwana 8 kafin rantsuwa

Zababben shugaban kasar ya dawo bayan shafe mako guda a Turai.

Zababben shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya dawo Najeriya kwanaki takwas kafin rantsar da shi a matsayin babban kwamandan sojojin tarayyar Najeriya.

Shugaban kasar mai jiran gado ya dawo Najeriya ne a ranar Asabar bayan mako daya a Turai.

Tafiyarsa ta baya-bayan nan ta tayar da kura, inda wasu rahotanni ke cewa yana fama da wata cuta da ba a bayyana ta ba.

Sai dai Tunde Rahman, mai magana da yawunsa, ya ce ya tafi kasar waje ne domin hutawa kafin rantsar da shi a ranar 29 ga watan Mayu.

A yayin da yake kasar waje, Tinubu ya gana da Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP da tsohon Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II.

Tattaunawar dai ta tayar da kura , inda wasu jiga-jigan jam’iyyar APC a Kano suka yi barazanar janye goyon bayansu ga zababben shugaban kasar idan ya bai wa tsohon gwamnan jihar mukami a gwamnatinsa.

Shi ma Gwamna Abdullahi Ganduje Kano ya koka a cikin wani sakon murya da ya karade kafafen yada labarai.

Amma Ganduje yana cikin manyan jiga-jigan da suka je filin jirgin Abuja domin tarbar Tinubu.

Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ahmad Lawan, mataimakin zababben shugaban kasa, Kashim Shettima, da Godswill Akpabio, na daga cikin wadanda suka tarbi Tinubu.

Zababben shugaban ya dawo ne a daidai lokacin da guguwar rikicin zaben shugabannin majalisa ta 10 ke kara kamari.

A yayin wata zanga-zangar da wasu 2yan takara suka yi, Sanata Abdullahi Adamu, shugaban jam’iyyar APC na kasa, ya ce za a sake duba jerin sunayen shugabannin majalisar dokokin kasar nan, amma ba a dauki matakin da Tinubu ya bayar ba.