✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Sakacin kasashen Turai ne ya sa har Rasha ta mamaye mu – Shugaban Ukraine

Ya ce da an kakaba wa Rasha takunkuman da wuri, watakila da ba ta mamaye kasarsa ba

Shugaban Kasar Ukraine, Volodymyr Zelensky ya zargi kasashen Turai da yin sakaci wajen kakaba wa kasar Rasha takunkumi tun da wuri don hana ta mamayar da take yi wa kasarsa a yanzu.

Zelensky ya ce kamata ya yi a ce sun sanya takunkuman tun kafin ta mamaye kasar ta yadda za su zama na gargadi, ba na fargar jaji ba, bayan an kaddamar musu da hare-haren.

A wani jawabinsa da aka yada ta bidiyo, Shugaba Zelenskyy ya shaida wa Tarayyar Turai cewa hatta sanya takunkumi a kan kamfanin da ke tunkuda iskar gas daga Rasha zuwa Jamus na Nord Stream 2, shi ma an yi shi a makare.

Jawabin nasa na zuwa ne bayan kasar ta Ukraine ta zargi dakarun Rasha da yi wa ’yan kasarta kimanin 400,000, ciki har da kananan yara 84, kofar rago a kasar.

A cewar Shugaban, “Game da batun Tarayyar Turai kuwa, muna godiya. Kun kakaba takunkumai, kuma sun taimaka sosai, amma sun dan zo a makare.

“Kamata ya yi a ce tun kafin ta kaddamar da hare-haren aka dauki matakan, da ba za ma ta kai ga kawo mana hare-haren ba. Akwai yiwuwar su ja da baya a lokacin,” inji Zelenskyy.

Ukraine dai ta nemi shiga kungiyar Tarayyar Turai, inda Shugaban a cikin jawabin nasa ya roke ta da ta gaggauta amincewa da bukatar tasu.

A wani labarin kuma, Shugaban Amurka, Joe Biden, ya ce kungiyar kawancen tsaro ya NATO za ta dauki matakin da ya dace muddin Rasha ta yi amfani da makamai masu guba a Ukraine.