✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Rashin tsaro: Kungiyar Izala ta umarci limamai su yi Alkunut

JIBWIS ta ce matsalar tsaro a Najeriya bukatar a koma ga Allah a nemi dauki.

Kungiyar Jama’atu Izalatil Bid’ah Wa Ikamatis Sunnah (JIBWIS) ta umarci lamamai su fara yin addu’ar Alkunut a salloli don Allah Ya kawo karshen matsalar tsaro a Najeriya.

Shugaban JIBWIS na Kasa, Shaikh Abdullahi Bala Lau ya bayar da umarnin, inda ya ce tabarbarewar sha’anin tsaro a Najeriya na bukatar jama’a su koma ga Allah su tuba gare shi.

A makon jiya wasu masallatan Juma’a sun fara gabatar da addu’ar ta Alkunut wadda ake yi idan aka samu bullar annoba ko wata matsala da ta addabi jama’a.