✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Najeriya ta koma ta 31 a jadawalin FIFA

Najeriya ta fara wannan shekarar ne a ta 32.

Najeriya ta koma ta 31 a jerin kasashe mafi kwarewa a kwallon kafa da Hukumar Kwallon Kafa ta Duniya fitar.

Hakan na zuwa duk da tawagar ta Super Eagles ta lallasa Sao Tome and Principe da ci 10-0, a wasan share fage na gasar cin Kofin Afirka.

Sai dai Super Eagles wadda ta nada sabon koci, Jose Peseiro ta ci gaba da zama ta hudu a Afirka.

Najeriya ta fara wannan shekarar ne a ta 32, inda ta samu ci gaba bayan da ta dawo na 30 a watan Maris, kafin ta kara sauka zuwa ta 31 a jadawalin na FIFA.

Senegal wadda ita ce ta daya a Afrika ta dawo ta 18 a teburin duniya, daga ta 22 a watan Maris.

Sai dai Brazil ta kara bai wa Belgium rata a matsayin ta daya, yayin da Argentina ta sauko da Faransa daga ta uku.