✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Najeriya ce ta 18 a gasar tsere da tsalle-tsalle ta Duniya

Darajar Najeriya ta karu a idon duniya.

Najeriya ce ta zo ta 18 a cikin jerin kasashe 43 da suka shiga gasar tsere da tsalle-tsalle ta duniya da aka yi a Jihar Oregon da ke kasar Amurka.

Najeriya ta taka wannan rawar ce a lokacin da ake tsaka da fargabar cewar ba za ta tabuka komai ba a gasar baki daya.

Nasarar da ’yar tseren Najeriya, Tobi Amusan ta samu na lashe gasar gudun mita 100 mai gajeren zango, gudun da ta kammala shi a dakika 12 da digo 12, ya sa ta zo daya a duniya, wanda ya hakan fito da sunan kasar.

Amusan ita ta ciwo wa Najeriya lambar zinarenta na farko a gasar, da har Shugaba Muhammadu Buhari ya jinjina mata tare taya ta murna.

Sai kuma Brume, wacce ta yi rawar gani a gasar tsalle mai dogon zango wacce ta samar wa kasar lamabar azurfa.

A karshen gasar wasannin baki daya, Najeria ta zo ta hudu a nahiyar Afirka. Yayin da ta ke bin bayan kasashen Kenya da Habasha da kuma Uganda.

A Nahiyar Afirka, kasar Habasha ce ke kan gaba a matsayi na 2 da lambar zinare 4, yayin da Kenya ta zo ta 3 nahiyar.

Kasar Uganda ita ce ta zo ta 14 a jerin kasashen da ke da yawan lambobin da suka ci a gasar.

Mai masaukin baki Amurka, ita ta lashe lambar gwal 13 wanda ya kai jimillar lambobin da ta samu na azurfa da tagulla 33, fiye da kowacce a duniya a gasar.

Gasar da aka soma a ranar 15 ga wata, an kare ta ce a ranar Lahadi, 24 ga watan Yuli.