Rundunar Sojin Kasa ta Najeriya ta ce ta gano sansanonin ’yan ta’adda guda biyu a mayankar Deidei da kauyen Dukpa da ke Gwagwalada a yankin Babban Birnin Tarayya Abuja.
Dakarun rundunar sun kuma kama ’yan ta’adda takwas da makamai da dama yayin wani samame da suka kai musu.
- Manyan ayyukan Buhari sun nuna inda basukan da yake ciyowa ke tafiya — Fashola
- An bankado ma’aikatan bogi 268 a Babbar Kotun Kogi
Sabon Daraktan Yada Labarai na rundunar, Manjo-Janar Musa Dan-Madami ne ya bayyana hakan a hedkwatar tsaro ta kasa da ke Abuja, ranar Alhamis.
Daraktan ya kuma ce sun kwato bindigogi kirar AK-47 guda biyar da manyan bindigogi guda uku da adduna da wukake da albarusai da kuma Tabar Wiwi mai yawa a hannun mutanen.
Idan za a iya tunawa, a ’yan makonnin da suka gabata, ’yan ta’adda sun kashe sojoji shida a yankin Bwari na Abujar, lamarin da ya jefa tsoro a zukatan mazauna Babban Birnin.
Kodayake akwai rade-radin cewar mayakan kungiyar Boko Haram da na ISWAP na da sansanoni a yankin, amma sanarwar sojojin ta kara tabbatar da labarin.
Da ya juya kan sauran aikace-aikacen rundunar kuwa, Manjo-Janar Musa ya ce dakarunsu na samun gagarumar nasara a jihohin Arewa maso Yamma da Arewa Gabas da Arewa ta tsakiya.