✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

‘Masu garkuwa da Kwamishinan Neja na neman N500m’

Rahotanni sun ce tun da safe ake ta taro kan matsalar tsaro a Jihar.

Wadanda suka yi garkuwa da Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Neja, Muhammad Sanni Idris, sun bukaci a ba su Naira miliyan 500 a matsayin kudin fansarsa.

Aminiya ta rawaito cewa an sace Kwamishinan ne a mahaifarsa da ke Babban Tunga a Karamar Hukumar Tafa ta Jihar, da sanyin safiyar Litinin.

Wata majiya ta shaida wa wakilinmu a Minna, babban birnin Jihar cewa tuni ’yan bindigar suka fara tuntuba ta waya domin a fara ciniki.

“Suna neman a ba su N500m, yayin da taron majalisar tsaron Jihar da Mataimakin Gwamnan ya jagoranta bai jima da kammala ba a Gidan Gwamnati, amma babu cikakkun bayanai a kai,” inji majiyar.

Rahotanni sun ce tun da safe ake ta taro kan matsalar tsaro a Jihar.

Sai dai har yanzu babu wani tabbaci a hukumance daga gwamnati kan bukatar ’yan bindigan.