✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Malaman firamare sun janye yajin aiki a Abuja

Za a jinkirta jarabawa domin a kammala darussan da aka dakatar saboda yajin aikin

Malaman makarantun firamare a Abuja sun janye yajin aikin da suka shafe mako biyu suna gudanarwa.

Da farko malaman sun shiga yajin ne saboda hukumomin birnin tarayya sun ki aiwatar da karin albashin da suka cancanta bayan an yi musu karin matsayi.

Shugaban Kungiyar Malamai (NUT) reshe Kubwa, Kwared Ameh Baba, ya tabbatar wa wakilinmu cewa an janye aikin ne a ranar Laraba, kuma nan take ake sa ran dalibai su koma makarantu.

Ya ce sun janye yajin aikinne bayan Ministan Birnin Tarayya, Muhammad Musa Bello da Sanatanta, Philip Aduda sun sanya baki domin yi wa tufkar hanci.

Kwamred Ameh, ya bayyana takaicinsa kan yadda shugabannin kananan hukumomin Birnin Tarayya ke yi wa harkar ilimin yara rikon sakainar kashi.

“Abin takaici shi ne ana cikin wannan yajin aikin, mutum uku daga cikin suka tafi Dubai kuma har yanzu ba su dawo ba, watakila sai bayan bukukuwan Kirsimeti”, inji shi.

Ya ce kungiyar za ta nemi a jinkirta lokacin fara jarabawa da aka tsara farawa ranar 5 ga watan Disamba, domin malamai su damu damar kammala darussan da ba su yi wa dalibai ba saboda yajin aikin.

A ranar 24 ga watan Nuwamba, takwarorinsu na makarantun sakandare suka janye yajin aikinsu na gargadi na kwana biyar.