✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Makarantu 62,000 na fuskantar barazanar tsaro

Bincike ya gano makarantun gwamnati ne suka fi fusknatar barazanar.

Hukumar tsaro ta ‘Civil Defence’ (NSCDC), ta ce makarantu 62,000 a fadin Najeriya na fuskatar barazanar tsaro.

Kwamanda-Janar na NSCDC, Ahmed Audi ya ce an gano hakan ne bayan wani bincike da hukumar ta gudanar kan yanayin tsao a makarantun kasar.

“Mun yi bincike kan hadarin da makarantu a fadin kasar nan ka iya fadawa sakamakon matsalar tsaro, shi ya sa muka bullo da sabbin matakan tsaron su.

“Binciken ya gano akwai makarantu sama da 81,000 a Najeriya amma abun mamaki shi ne 62,000 ba su da kariya ko tsaro na zahiri kamar katanga da sauransu.

“Hakan na nufin yara suna cikin hadarin hari a kodayaushe kuma yawancin makarantun na gwamnati ne,” a cewarsa.

Da yake jawabi yayin kaddamar da sabbin motoci 200 ga kananan jami’an hukumar a Abuja ranar Talata, Kwamanda-Janar din ya ce ya zama dole a kara himma wajen kawo sabbin matakan kare makarantu a Najeriya.

Audi ya bayyana cewar hukumar ta fara shirye-shiryen gabatar da kayan aikin tsaro na sanya ido a kan kayan gwamnati a fadin kasar.

“Najeriya na fama da rikice-rikice; Mun gano cewar dole ne sai an koma tushe don yin aiki cikin fikira da bullo da sabbin hanyoyin dakile matsalolin tsaro”.

Ya yi kira da a bullo da sabbin hanyoyin yaki da ta’addanci ciki har da karfafa wa jami’an tsaro gwiwa duba da yadda matsalar ke kara ta’azzara.