✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Magidancin da ya nemi yada hoton tsiraicin matarsa ya shiga hannu

Tsohon yana kuma barazana ga matar tasa da suka samu sabani da ita.

Wani dattijo mai shekaru 60 ya gurfana gaban kotu saboda barazana ga rayuwar matarsa da kuma kurarin yada hotunan tsiriacinta.

Muutm ya shiga hannu ne bayan ya tuttura wa matar tasa sakonnin barazaar ta wayanta, bayan wani sabani da ma’auratan suka samu.

Bayan gudanar da bincike ne ’yan sanda suka cafke magidancin, suka gurfanar da shi a gaban Kotun Majistare da ke zamanta a Ikeja, bisa zarginsa da tada hankalin matar da kuma neman ta da zaune tsaye.

Mai gabatar da kara, ASP Kehinde Ajayi, ya shaida wa kotu cewa mutumin ya aikata laifin ne a ranar 11 ga Disamba, 2020, a Ikeja.

Ya ce laifukan sun saba da Sashe na 168 da 56 na Dokar Manyan Laifuka ta Jihar Legas ta 2015, wanda ya tanadi daurin shekara daya a gidan yari, ga wanda ya aikata laifi irin wannan.

Sai dai wanda ake tuhumar ya musanta aikata lafin da ake zargin sa da aikatawa.

Alkalin kotun, Misis A.O Ajibade, ta bayar da belin wanda ake karar a kan kudi N100, 000 tare da mutane biyu da za su tsaya masa.

Ta kuma dage sauraron shari’ar zuwa ranar 11 ga watan Fabrairu, 2021.