✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Mafarauta sun ƙwato shanu daga hannun Boko Haram a Borno

Mafarautan sun suna neman ragowar 'yan ta'addan da suka tsere.

Wasu mafarauta a unguwar Ruga da ke Ƙaramar hukumar Mafa a Jihar Borno, sun yi nasarar ƙwato shanu 10 da ’yan Boko Haram da ISWAP suka sace.

Rahoton rundunar ’yan sandan jihar daga Kakakin ‘yan sandar Nahum Daso ne ya  bayyana cewa, mafarautan sun samu labari daga wasu manoma cewa ’yan ta’adda sun wuce zuwa dajin kusa da unguwar Ruga ɗauke da makamai da kuma shanu.

Ɗaya daga cikin mafarautan ya ce sun haɗu gaba ɗaya, sannan suka kai wa ‘yan ta’addan farmaki a ranar 16 ga watan Yuli, 2025.

Ya ce, “Da muka hango su ɗauke da shanun da suk sace, sai muka farmake su da makamai. Sun gudu da wasu shanun amma mun samu nasarar ƙwato guda 10.”

An tafi da shanun da aka ƙwato don a adana su yayin da ake ci gaba da neman sauran dabbobin da kuma ‘yan ta’addan da suka tsere.

‘Yan sanda sun ce za su miƙa shanun da aka samu zuwa hukumar kula da kiwon dabbobi ta Jihar Borno (BORMA) bayan kammala bincike.