✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kwamishinan Noma na Jihar Sakkwato ya rasu

Kwamishina na hudu ke nan da ya rasu a Gwamnatin Aminu Tambuwal.

Kwamishinan Noma na Jihar Sakkwato, Muhammad Arzika Tureta, ya rasu da safiyar Litinin.

Arzika wanda shi ne tsohon Shugaban Jam’iyyar PDP na Jihar Sakkawto ya rasu yana da shekara 62, a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo bayan fama da rashin lafiya.

Muhammad Arzika,  shi ne mutum na hudu a cikin Kwamishinonin Gwamna Aminu Waziri Tambuwal da suka rasu.

Sauran su ne Kwamishinan Kasa da Gidaje, Jeli Abubaka III; Kwamishinan Harkokin Cikin Gida, Surajo Gatawa;  sai Kwamishinan Sadarwar Zamani, Nasiru Zarumai.

A baya Arzika ya rike mukamin Kwamishinan Ilimi a zamanin Gwamna Aliyu Magatakarda Wamakko.

Ya kasance dan Majalisar Jihar Sakkwato a karkashin rusasshiyar jam’iyyar NRC kuma tsohon dan Majalisar Wakilai ne mai wakiltar mazabar Bodinga/Dange-Shuni/Tureta a karkashin jam’iyyar PDP.

Ya rasu ya bar mata biyu da ’ya’ya bakwai da jikoki da dama.