✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Kano ta Tsakiya: Laila Buhari ce ’yar takarar PDP —Kotu

Kotun Daukaka Kara ta soke takarar Danburam Nuhu da Jam’iyyar PDP ta gabatar a kujerar Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya

Kotun Daukaka Kara a Kano karkashin jagorancin Mai Shari’a Itan Mbaba ta soke takarar Danburam Nuhu da Jam’iyyar PDP ta gabatar a kujerar Sanata mai wakiltar Kano ta Tsakiya.

Kotun ta amince da zaben fidda-gwani da jam’iyyar ta gudanar, karkashin shugabancin Shehu Sagagi, wanda ya fitar da Laila Buhari a matsayin ’yar takarar.

Haka kuma kotun ta umarci Hukumar Zabe ta Kasa (INEC ) da ta soke sunan Damburam Nuhu tare da maye gurbinsa da na Laila Buhari a matsayin ’yar takarar Kano ta Tsakiya a PDP.

A anar 26 ga watan Satumba ne wata Babbar Kotun Tarayya da ke Kano ta yi watsi da karar saboda rashin hurumin shari’a, bisa hujjar cewa an shigar da karar ne a Kano maimakon Abuja, sabanin tsarin Majalisar Shari’a ta Kasa (NJC) kan al’amuran da suka shafi kararraki kafin zabe.

Amma a hukuncin da Mai Shari’a Itang Mbaba ya yanke a ranar Laraba, Kotun Daukaka Kara ta yi watsi da hukuncin da nabbar kotun, wanda ta ce kuskure ne yin watsi da karar a kan wannan batu.