✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

IPOB: Gwamnonin Arewa sun yi tir da kisan Gulak

Kungiyar ta yi Allah wadai da kisan gillar da aka yi wa Ahmed Gulak a Imo.

Kungiyar Gwamnonin Arewa (NGF), ta bayyana kisan tsohon Mashawarci na Musamman ga Shugaban Kasa Goodluck Jonathan kan Harkokin Siyasa, Ahmed Gulak, a matsayin abin takaici mafi girma kuma abin Allah wadai.

A martaninsa game da kisan, Shugaban Kungiyar kuma Gwamnan Jihar Filato, Simon Bako Lalong, ya ce abin bakin ciki ne kuma abun kyama.

“Mummunan abu ne wanda dole a yi tir da shi gaba daya,” inji shi.

Lalong ya ce dole ne a kalli kisan Gulak a matsayin laifi mafi muni, sannan ya yi gargadi cewa siyasantar da lamarin ka iya haifar da mummunan tashin hankali a kasa.

Ya ce rahoton da ’yan sanda suka bayar na ganowa da kuma kashe wadanda ake zargi da kisan marigayin dan siyasar, abun a yaba ne.

Shugaban kungiyar gwamnonin ya bukaci jama’a da su rika karfafa wa jami’an tsaro gwiwa don samun damar dakile ayyukan ta’addanci a Najeriya baki daya.

Ahmed Gulak ya gamu da ajalinsa ne yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa filin jirgin sama a Jihar Imo, inda ’yan bindiga da ake zargin ’yan haramtacciyar kungiyar IPOB ne suka harbe shi har lahira, da safiyar ranar Lahadi.