✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

INEC ta ci gaba da tattara sakamakon zabe a Abuja

A zaman da ka ci gaba a safiyar Litinin ake sa ran karbar sakamakon zaben shugaban kasa daga jihohi 35 da kuma Birnin Tarayya.

Hedikwatar Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ci gaba ta karba da kuma bayyana sakamakon shugaban kasa bayan ta dakatar da aikin a ranar Lahadi da dare.

An ci gaba da aikin ne a Cibiyar Taro ta Kasa da Kasa da ke Abuja, karkashin jagorancin shugaban INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, wanda shi ne baturen zabe na kasa.

A zaman da ka ci gaba a safiyar Litinin ake sa ran karbar sakamakon zaben shugaban kasa daga jihohi 35 da kuma Birnin Tarayya.

Idan ba a manta ba an dage zaman ne daga ranar Lahadi bayan da INEC ta karbi sakamakon zaben shugaban kasa na Jihar Ekiti.

Ana sa ran bayan nan ne za a sanar da wanda ya yi nasara a zaben da aka gudanar a ranar Asabar, 25 ga watan Fabrairu 2023.

Jam’iyyu hudu ne ake gani suna kan gaba a zaben shugaban kasar wanda shi ne karo na bakwai daga lokacin da Najeriya ta sake dawowar Najeriya kan tsarin mulkin dimokuradiyya shekarar 1999.