✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

INEC ta ba Fintiri shaidar lashe zaben Gwamnan Adamawa

Ya karbi shaidar ce a hedkwatar hukumar da ke Abuja

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ba Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri shaidar lashe zaben Gwamnan Jihar a karo na biyu.

INEC ta ba Fintirin shaidar ce a Abuja, kwana daya bayan ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben da ta bayyana sakamakonsa.

Gwamna Fintiri ya karbi shaidar ce tare da mataimakinsa, Farfesa Kaletapwa Farauta, wajen misalin karfe 5:00 na yammacin Laraba a hedkwatar hukumar ta kasa da ke Abuja.

Ya sami nasarar ce a karkashin jam’iyyar PDP, bayan ya lashe zaben da ya sha fama da dambarwa iri-iri, inda ya kayar da babbar abokiyar hamayyarsa ta jam’iyyar APC, Sanata Aisha Dahiru Binani.

A karshen zaben dai, ya sami kuri’a 430,861 ne, inda ita kuma Binani ta sami kuri’a 398,738.