Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta ba Gwamnan Jihar Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri shaidar lashe zaben Gwamnan Jihar a karo na biyu.
INEC ta ba Fintirin shaidar ce a Abuja, kwana daya bayan ta bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben da ta bayyana sakamakonsa.
Gwamna Fintiri ya karbi shaidar ce tare da mataimakinsa, Farfesa Kaletapwa Farauta, wajen misalin karfe 5:00 na yammacin Laraba a hedkwatar hukumar ta kasa da ke Abuja.
Ya sami nasarar ce a karkashin jam’iyyar PDP, bayan ya lashe zaben da ya sha fama da dambarwa iri-iri, inda ya kayar da babbar abokiyar hamayyarsa ta jam’iyyar APC, Sanata Aisha Dahiru Binani.
A karshen zaben dai, ya sami kuri’a 430,861 ne, inda ita kuma Binani ta sami kuri’a 398,738.