✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

El-Rufai ya kaddamar da rushe gidaje a Zariya

Mazauna yankin sun koka tare da neman dauki daga gwamnatin jihar.

Gwamnatin Jihar Kaduna ta kaddamar da rusa dubban gidajen da ke bayan Kwalejin Tukin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAT) da ke Zariya a ranar Litinin.

Rusau din ya biyo bayan kwashe shekaru ana tafka shari’a tsakanin hukumar kwalejin da masu gidajen da take zargi da yin kutse a filin kwalejin.

Wasu daga cikin masu gidaje da Aminiya ta zanta da su kan lamarin sun bayyana cewa suna rokon gwamnati da ta tausaya ta tallafa musu.

Yadda aka rushe gidajen mazauna yankin. (Hoto: Aliyu Babankarfi).

Al’ummomin sun yi kira da cewa su ’yan kasa ne ba baki ba kuma sun bi duk dokokin da suka dace kafin su yi gini a filayen nasu da saya suka yi.

Daya daga cikin motocin da suke aikin rushe gidajen. (Hoto: Aliyu Babankarfi).

Aminiya ta ga yadda mutanen da aka rushe gidajen nasu ke ta kwashe kayayyakinsu da kuma balle wasu daga cikin kayan rufin gidajensu da kansu.

Wannan ba shi ne karo na farko da gwamnatin jihar karkashin jagorancin Nasir El-Rufai ke rushe wuraren da mutane suke zaune ba bisa ka’ida ba a jihar.