Gwamnatin Tarayya ta ce ta fara yunkurin cire ’yan Najeriya miliyan 40 daga kangin talauci nan da shekara biyu masu zuwa.
A cewarta, za ta yi hakan ne ta hanyar shirinta na farfado da tattalin arziki da rage radadin talauci bayan annobar COVID-19 mai suna NG-CARES.
- ‘Har da dan kasar waje a cikin fasinjojin da aka sace a jirgin kasan Kaduna’
- 2023: Osinbajo ya ayyana tsayawa takarar Shugaban Kasa
Jami’in shirin na kasa, Abdulkarim Obaje, ne ya bayyana hakan a Ibadan, babban birnin Jihar Oyo ranar Lahadi, yayin bikin rufe wani taron kara wa juna sani kan shirin.
An dai gudanar da taron ne a Ibadan, kuma ya samu halartar mutum 440 daga Jihohi 36 da ma Babban Birnin Tarayya Abuja.
Daga cikin wadanda aka horar din har da wadanda za su rika kula da shirin a sassa daban-daban na Najeriya.