✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Cire tallafi: Kwanan nan farashin mai zai sauko – NNPC

Ya ce 'yan Najeriya su daina fargaba

Shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPC), Mele Kyari, ya bukaci ’yan Najeriya su sha kuruminsu, saboda kwanan nan farashin man fetur zai sauka bayan cire tallafi.

Ya ce gasar da za a rika samu tsakanin manyan ’yan kasuwar mai zai sa tilas farashin man ya sauka, sabanin fargabar da ake da ita a yanzu ta tashin farashin.

Aminiya ta rawaito cewa a ’yan kwanakin nan dai layuka sun fara dawowa a gidajen man Najeriya sakamakon cire tallafin mai da kuma karin farashi.

A wata hirarsa da gidan talabijin na Arise ranar Alhamis, Mele Kyari ya ce janye tallafin zai haifar da sabbin ’ya kasuwa da zai sa man ya yi sauki sannan ya magance kakagidan da wasu ’yan kasuwar suka yi.

A cewarsa, “Amfanin cire tallafin shi ne za a sami sabbin ’yan kasuwa da za su shigo harkar wadanda a baya ba sa cikinta, kuma hakan zai sa abubuwa su yi sauki.”