✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Bukayo Saka ya tsawaita yarjejeniyar zama a Arsenal

Saka mai shekara 21 ya yi karawa 178 a kungiyar Emirates.

Bukayo Saka ya saka hannu kan yarjejeniyar mai tsawo da zai ci gaba da taka leda a Arsenal.

Dan wasan tawagar Ingila, ya ci kwallo 14 a Gunners a kakar nan, ya kuma bayar da 11 aka zura a raga.

Saka mai shekara 21 ya yi karawa 178 a kungiyar Emirates, ya kuma buga wa Arsenal dukkan wasannin Premier League a kaka biyu.

Tun farko kwantiragin Saka zai karkare a Arsenal a karshen kakar 2023-24, inda a yanzu ya tsawaita yarjejeniyar zuwa 2027.

Arsenal, wadda take ta biyu a teburin Firimiyar Ingila za ta karbi bakuncin Wolverhampton a wasan karshe a kakar bana.

Manchester City ce ta dauki kofin babbar gasar tamaula ta bana, bayan da Arsenal ta barar da damar lashe kofin kakar nan a karon farko tun bayan 2003/04.

Mikel Arteta ya ce zai yi kokari ya rike manyan ‘yan wasan Gunners, domin kalubalantar gasar zakarun Turai ta Champions League ta badi.