✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari zai kaddamar da gidaje 500 a Borno

A karo na uku Shugaba Buhari zai kai ziyarar aiki Maiduguri, babban birnin Jihar Borno.

Shugaban Kasa Muhammad Buhari zai kai ziyara Maiduguri, babban birnin Jihar Borno domin kaddamar da wasu ayyuka da aka kammala a ranar Alhamis.

Karo na uku ke nan da shugaban kasar zai kai ziyara Jihar Borno, bayan zuwan da ya yi a watan Yuni da kuma watan Disamban 2021.

Ana sa ran a yayin ziyarar, Buhari zai kaddamar da gidajen malamai a unguwar Bulunkutu da kuma gidaje 500 da gwamnan jihar, Babagana Zulum ya gina wa ’yan gudun hijira a yankin Molai.

Zai kai ziyarar ban girma ga Fadar Shehun Borno, Umar Ibni Elkanemi.