✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Buhari ya nada Solomon Arase Shugaban Hukumar Harkokin ’Yan Sanda

Nadin zai tabbata ne bayan Majalisar Dattawa ta amince da hakan.

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya nada tsohon Sufeto-Janar na ’Yan Sanda, Solomon Arase, a matsayin sabon Shugaban Hukumar Harkokin ’Yan Sanda ta Najeriya (PSC).

Sai dai nadin nasa zai tabbata ne bayan Majalisar Dattawa ta amince da hakan.

Wasikar da Buhari ya aike wa Majalisar wadda Shugabanta, Sanata Ahmad Lawan, ya karanto yayin zamansu na ranar Talata, ta nuna Buhari ya nada Arase ne ta yin madogara da sassa na 153 (1) da 154 (1) na Kundin Tsarin Mulki wanda aka yi wa gyara.

Idan nadin ya tabbata, Arase zai zama ya gaji Musiliu Smith a mukamin, wanda ya yi murabus a bara cikin yanayi  mai rikitarwa

Kafin nadin nasa, shi ne shugaban sashen tattara bayanan sirri na Hukumar ’Yan Sandan Najeriya da Hukumar Leken Asiri da Binciken Manyan Laifuka.

Arase ya zama Sufeto-Janar na ’Yan Sanda a 2015 karkashin gwamnatin tsohon Shugaban Kasa Goodluck Jonathan bayan cire Suleiman Abba da ya yi a mukamin saboda rashin biyayya.