✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

Atiku zai garzaya kotu kan zaben shugaban kasa

Atiku, wanda ya zo na biyu a zaben shugaban kasa, ya ce zaben 2023 shi ne mafi muni a tarihin Najeriya

Dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce zai kalubalanci sakamakon zaben shugaban kasa na 2023 da aka gudanar a ranar Asabar a kotu.

Atiku, a wani taron manema labarai a ranar Alhamis a Abuja, ya ce matakin bai shafe shi ba kai-tsaye, amma zai yi haka ne don dimokuradiyyar Najeriya.

“Zaben da aka gudanar a karshen mako babu gaskiya a cikinsa. Binciken farko ya nuna cewa shi ne zabe mafi muni da aka taba gudanarwa tun bayan dawowar mulkin dimokuradiyya a 1999.

“Magudi da zamba da aka yi a wannan zaben, ba a taba yin irinsa ba a tarihin kasarmu.

“Na kasa fahimtar dalilin da ya sa aka yi gaggawar bayyana sakamakon zaben duk da korafe-korafen da aka yi game da shi,” in ji shi.

Ya ce tuni ya tuntubi shugabannin jam’iyyarsa ta PDP da ’yan Najeriya daga bangarori daban-daban kan sakamakon zaben, kuma suka cimma matsayar garzaya wa kotu.

Atiku ya ce masu sanya ido na cikin gida da na waje sun tabbatar da akwai kura-kurai a zaben.

Ya ce ya yi imanin cewa wannan ba shi ne alkawarin da Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi ba, kuma bai makara ba ya gyara barnar da aka yi a zaben.

Atiku Abubakar ya zo na biyu a zaben da aka gudanar bayan shan kaye a hannun Tinubu na jam’iyyar APC.