✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

An kama mutumin da ya yi barazanar gayyatar ’yan awaren IPOB zuwa Legas

An nemi kama shi a fadarsa, amma sai ya tsere zuwa wani otal.

Jami’an Hukumar Tsaro ta Farin Kaya DSS sun kama jagoran kabilar Igbo mazauna rukunin gidajen Ajao a Legas, Fredrick Nwajagu.

Fredrick Nwajagu ya yi barazanar gayyatar ’yan kungiyar aware ta IPOB zuwa Legas don kwato wa al’ummar Igbo kadarorinsu a jihar.

Bayanai sun bayyana cewa, an kama jagoran Igbo ne da safiyar Asabar a wani samamen hadin gwiwa tsakanin jami’an DSS da ’yan sanda.

Aminiya ta ruwaito cewa, jami’an tsaron sun nemi kama shi a fadarsa, amma sai ya tsere inda suka rika bin sawu har suka kama shi a wani otal.

A cikin wani hoton bidiyo da aka fitar ranar Juma’a a shafin Twitter, Mista Nwajagu mai shekara 49 ya yi barazanar gayyatar ’yan awaren IPOB zuwa Jihar Legas domin kare ’yan kabilar Igbo mazauna jihar daga hare-haren da ya ce ana kai musu.