✕ CLOSE Noma Da Kiwo Hotuna Kiwon Lafiya Girke-Girke Sana'o'i Kimiyya da Kere-Kere Ra'ayin Aminiya Ra’ayoyi Rahoto
Click Here To Listen To Trust Radio Live

A dakatar da shugaban makarantar da aka kai wa masu hijabi hari —MURIC

MURIC ta bukaci ta rufe makarantar domin hana tashin fitina

Kungiyar Kare Hakkin Musulmi (MURIC) ta bukaci a dakatar da Shugaban Makarantar Baptist High School, tare da rufe makarantar a sakamakon harin da aka kai wa dalibai masu sanya hijabi.

MURIC ta yi kiran ne bayan harin da ’yan daba da jami’an tsaro suka kai wa dalibai mata Musulmi a makarantar a lokacin da suke gudanar da zanga-zangar lumana ta neman ’yancinsu na sanya hijabi a ranar Alhamis.

MURIC ta kuma yi kira da a rufe makarantar da ke yankin Ijagbo na Karamar Hukumar Oyun ta Jihar Kwara, domin dakile tashin fitina, bayan harin ya yi sanadiyyar jikkata mutum hudu, har kaa kwantar da dayansu a asibiti.

Daraktan MURIC, Farfesa Ishaq Akintola, ya yi Allah wadai da harin, yana mai cewa ya kamata a dakatar da shugaban makarantar ba tare da bata lokaci ba.

Ya ce, “Duk da cewa ana rade-radin cewa an kashe mutum daya, ba za mu yi magana a kai ba, har sai mun samu cikakken bayani daga reshenmu na Jihar Kwara.

“Mun yi tir da harin kidahumanci da aka kai wa kananan ’yan mata da ke zanga-zangar lumana ba tare da daukar wani makami ko tayar da yamutsi ba.

“Zanga-zangar lumana halastacciyar hanya ce ta bayyana korafi ko nuna rashin jin gamsuwa da wani, buddin aka gudanar da zanga-zangar cikin lumana,” a cewar Farfesa Akintola.